Wuraren da suka gurfana a gaban kotun sun haɗa da Domino’s Pizza, Jalsa Shop, FCMB Bank da Nasarawa Suya Spot, waɗanda ke kan titin Bompai a Kano. Binciken jami’an hukumar ya gano matsaloli da suka haɗa da ciyayi da suka yi yawa, zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, taruwar yanar gizo, tarkace da kayan da ba a buƙata, rashin isassun kwandunan shara da kuma rashin kula da tsaftar wuraren.
Kotun ta yanke wa wuraren hukuncin ɗaurin makonni biyu ko biyan tara, bisa tanadin dokokin tsaftar muhalli na jihar.

1
Manajan Daraktan REMASAB, Dr. Muhammad S. Khalil, ya yi kira ga masu gidaje, ‘yan kasuwa da kamfanoni da su ɗauki batun tsaftar muhalli da muhimmanci, tare da tabbatar da cewa wuraren kasuwancinsu suna cikin tsafta da tsari a kowane lokaci.
Ya kuma buƙaci jama’a da su rika zubar da shara yadda ya kamata, samar da kwandunan shara, share ciyayi, da tabbatar da cewa magudanan ruwa ba su toshe ba.
Kotun ta kuma jaddada cewa kiyaye tsaftar muhalli nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, yayin da REMASAB ta ce za ta ci gaba da aiwatar da dokokin tsaftar muhalli cikin adalci ga duk wanda ya karya ƙa’idojin.

2
Kotun, wadda Mai Shari’a Halima A. B. Wali ta jagoranta tare da Barrister Bahijja H. Aliyu, ta gudanar da zaman ne a ranar 11 ga Agusta, 2026.




