Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Dr. Mujahideen Aminuddeen, ya bayyana hakan cikin wani saƙon da ya aikewa Glob Hub, inda ya ce sabbin motocin da baburan za su taimaka wa jami’an hukumar wajen gudanar da ayyukansu cikin sauri da inganci a sassa daban-daban na jihar.

2
Dr. Mujahideen ya kuma gargadi masu aikata abubuwan da suka saba wa doka, tarbiyya da koyarwar addini da su shiga hayyacinsu, yana mai cewa hukumar ba za ta bari a ci gaba da aikata barna a jihar ba.
Ya ce Hukumar Hisbah za ta ƙara ƙaimi wajen tabbatar da zaman lafiya, kyawawan ɗabi’u da kare tarbiyyar al’umma, tare da ɗaukar matakan da suka dace kan duk wanda aka samu yana aikata abubuwan da suka saba wa dokokin jihar da ƙa’idojin al’umma.

1



