Tawagar za ta bibiyi yadda ɓangarorin biyu ke aiwatar da yarjejeniyar tare da duba matakan da ake ɗauka domin tabbatar da tsagaita wuta da dawo da zaman lafiya a yankunan da rikicin ya shafa.
Qatar ta ce sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar na daga cikin ƙoƙarin tabbatar da cewa yarjejeniyar ta haifar da zaman lafiya mai ɗorewa, tare da ƙarfafa amincewa tsakanin ɓangarorin da ke rikicin.





