Mai magana da yawun Ma鈥檃ikatar Harkokin Wajen Sin, Guo Jiakun, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar ranar Talata, 1 ga Satumba. Ya ce hanyoyi da hanyoyin sadarwa sun katse a yankin da iftila鈥檌n ya shafa, yayin da ake fargabar sake afkuwar wasu bala鈥檕鈥檌.
Guo Jiakun ya ce hukumomin kasar na yin duk mai yiwuwa wajen gano tare da ceto mutanen da suka bace, ciki har da 鈥檡an kasashen waje. Ya kuma ce ana tuntubar ofisoshin jakadancin kasashen waje da ke kasar Sin domin taimakawa wajen gano 鈥檡an kasashensu da suka bace.
Ya kara da cewa hukumomin Sin na ci gaba da ayyukan kai dauki da agaji, tare da kokarin magance matsalolin da iftila鈥檌n ya haifar, yayin da ake ci gaba da tantance halin da yankin ke ciki.




